Main menu

Pages


 Page 7&8


Oum Aphnan✍️



Bin bayansa Hajiya ladi tayi da sauri tana cigaba da masa magiya ,amma in ƙasa ta motsa to ya tanka ,oya oya ya shiga tattare tarkacensa ,kana ya kira wayan Yusuf fagachi ,ya gaya masa inda zaizo ya ɗaukesa.


Hajiya Binta kam sosai ta ƙullaci ƙawarta amma ta shanye bata nuna ta damu ba ,ta kai bilki inuwa ta ɗage mata kanta sama ta goge mata jinin .


Hajiya ladi kam a furgice taje bed room dinta ta ɗauki waya ta hau kiran layin Gimbiya Sauda ,saidai kira na uku kafin jakadiyarta ta ɗauka 


"Hello ranku shi daɗe ,Na ɗayo aiki...." Katse ta jakadiya tayi 


"Gimbiya na cikin baƙi ,bazata samu daman ɗaga waya ba"


Tsaki taja tayi cilli da wayar ,kafin ta ɗan goya hannunta a baya ta fara kewaye ɗakin 

"Ina sha'awar kyakkyawar matashin nan ,idan har na bari yabar mun gidan nan ,tamkar ƙwalele yayi mun,to yanzu ya zanyi?" 


Zabura tayi kawai ta nufi ɗakinsa daga ita sai ɓingilar riga mara hannu iya rabin ƙafa bai gama sauka mata ba ,ruwan silver yabi ya kwakkwanta a cuccuran tsokokin jikinta ,mirza handle din Kofar tayi tana kiran sunansa amma ba wani bayanin zai buɗe ,da sauri taje ta ɗauko master key ɗin gidan ,tana wani irin haki kamar wacce tayi gudu,saboda yanda budurwar zuciyarta take ƙara ƙawata mata kyawun sa ,da burin ta samu ya kulata a yau koda zai tafi ne ita dai.


Tana buɗe ƙofar ta maida duk ta rurrufe ta danna kanta cikin bedroom ɗinsa


A ruf da ciki ta gansa still kayan jikinsa dai sune a jikinsa 


Wani killing smile ta saki ,sannan ta dunfarosa gadan gadan 


Jin takunta yasa ya miƙe da sauri yayi zaman en bori akan katifan ,yana zazzaro ido cikin tsoro da furgici


Muryar ta a dishe ,cikin murya raɗa ²  ta kira sunan sa 


Hangame baki yayi ya kasa amsa ta, ya cigaba da zurawa sarautar Allah ido . 

Zube guiwoyinta tayi akan katifan da yake kwance ta cigaba da haurowa kansa ,saida tazo dab dashi kafin ya yunƙura kamar wanda aka mintsila ya miƙe zubur jikinsa ya ɗauki ɓari 


"Sadiƙu my boy ka taimaki momynka kaji ? Gani da dakon buƙatuwata don Allah karkacemun A'ah wlh in munyi babu mai ji ,sau ɗaya kawai! Wallh Allah ya jarabceni da matsananciyar sha'awarka in ka bani hadin kai zan uzzurawa Commissioner mijina sai yasa an maidaka makarantanka ...."


Miƙa mata hannu yayi alamar dakatarwa 


"Dakata!!! Ni kin isheni da surutanki da bana fahimta ,Ni dan iska ne aka gaya maki? Dallah matsa Ni da jikinki zubin na Aladai"


"Kataimaka mun Sadik in baka cini ba mutuwa zanyi yau din nan" 


Tazo da sauri zata cafke sa yayi saurin zillewa ya ƙumu da boglarin window a hannu ,da sauri ya saki ƙara "Ahshhhhh...ke ki mutu mana Ni ina ruwana ,wai wani masifa ne ya kawo Ni wannan gidan?"


"Masifan sona kuma sai ka soni sai ka cini dole"


"To zamu gani " ya fada yina juya baya yina cigaba da lailaya inda ya ƙume


Ba zato ta afka masa gaba-daya nan suka fara kici kici ,yina son ya kwaci kansa tana kokarin keta masa sutura ,daddagewa yayi ya kurma ihu ,don Abun yafi ƙarfinsa ta turmushesa ta haye ruwan cikinsa 


"Wayyo na shiga uku ku taimakeni ku kawo mun ɗauki fyaɗe zata mun wallahi" 


Gyara zamanta akansa tayi tana ƙoƙarin zuge zif ɗin rigarta "Ai baka sani ba ,duk wani wanda yake mun aiki a gidan nan tamkar mazaje nane ,damata ne ina darza ƙosashshe mu saki labule ,kaine kadai bare kuma yau zan zama influencer"


Numfashinsa dakyar yike jansa saboda nauyinta yayi tasiri akansa ko motsi bashi iyawa 


"Akwai ƙawarki a gidan kuma zan cigaba da ihu har sai ta san cewa ke fasiƙa ce"


"Ahaf itama ɗin dadiro ta ce ,so menene karkasa in cika kuma in na gama in gayyato ta itama ta kwashi lagwada"


Wahalalllen Numfashi yike saki ,wani gumi na tsatsafo masa ko ta ina ,jikinsa har ya fara saki ,shi tunda yike bai taɓa sanin irin wannan wahalar ba 


Shashafasa ta shiga yi tun daga dokin wuyarsa zuwa ƙasan kafaɗunsa ,zuruf ya cafki ,hannunta ya yanka mata wani irin kakkaifan cizo ya datse haƙoransa ,ihu take kurmawa na azaba jini na tsartuwa amma yaƙi saki 


Dukansa take iya ƙarfi ta da hannu 1 to amma ai shifa sojane baijin bugu ,kawai yaƙi sakin hannun duk da jinin dake fita 



Gwale muryarta ta yi tana ihu "Wayyo Allah zai tsinka mun jijiyoyin jini ,wayyo Azabaaaaa!" 


Murginewa tayi ta sauka a kansa nanko Allah ya taimake sa ya cikata ya miƙe .

Cikin layi ta kuma biyosa luuuuu zuciyarta a ƙeƙeshe gabaɗaya zina take hangowa a ranta 


Dunƙule hannunsa yayi ya shiga bata blow iya ƙarfinsa kamar ya sama wulli majiyin ƙarfi .


Warwas ta zube a wajen ya tattare kayansa ya saka sauri ² ya fice da gudu 


**** 

Su Hajiya Binta fa ,suna ƴan wanne?? 


Tana nan tana jinyar erta sai ga kiran CP 

Zumbur ta miƙe ta bar Bilkisu a wajen tayi saurin kanga wayar a kunne cikin muryar marasa gaskiya 


"Hellooo"

Baby girl yaya ,a'ina zamu haɗu,nidai gani a guest room din gidan nan "


"Shikenan ina zuwa " ko ƙara bi ta kan Bilkisu batayi ba ta wuce hanyar shashashancin ta 


Bilkisu da cikin sanɗa ta dinga bin bayan uwarta har ta ga inda ta shiga ,da sauri ta leƙa ta kafan ƙofa ,cp ta hanga tif da gajeren wando da farin singlet ya turo rusheshen ciki gaba ,uwarta na kan cinyarsa .


Rumtse ido tayi da karfi ,wasu hawaye Masu raɗaɗi suka shatato mata ,da baya da baya ta rinƙa tafiya idonta ya cika da hawaye sam bata sanin inda take jefa ƙafarta 


Karo tayi da jikin mutum ,tayi luuu wannan karon da sauri ya tarota ,ya watsa mata kallon ƙiyayya akan innocent face ɗin ta 


"Ƴar ƴan karuwai ,ƴan bariki ,mazinatan mata masu fasiƙanci ,maɗigo da shaye² ,ke kika ja uwarki ta mareni ko?....saina tarwatsa rayuwarki zakisan Kin shigo halarar Sadik sarki ,yanzu ki sani duk wani motsi naki ya dawo ƙarƙashin ikona sai nasa uwarki kuka akanki ,mu zuba ,wasan ba'a fara ba " 


Ya hankaɗeta da sauri gefe ,taje taga² zata faɗi ta maza ta dafa wani ƙarfe shikuma yayi wucewar sa cike da isuwa.

author-img
Talented Aurthor, blogger in fashion and YouTuber in habits, I am living in keffin Magaji Dan Yamusa, Nasarawa state Nigeria, I am specialist at any kind of webdesign,webdevelopment, graphics designer and video editing I can make inpossible to possible with my laptop

Comments

table of contents title