UNCLE NE complete hausa novel written by Ni’imerh Sulaiman Shu’aibu
Description
You are about to download UNCLE NE complete hausa novel written by Ni’imerh Sulaiman Shu’aibu released on 2022 just proceed with your download by following the below instruction.
Gabatarwa
Unguwar Masu kuÉ—i ce,Unguwa ce da babu wanda ya damu da rayuwar wani,Unguwa ce mai cike da Attajirai,Malamai,haÉ—i da Æ´an boko,Haka kuma Unguwa ce mai cike da Æ´an duniya wanda idanunsu suke a buÉ—e,basa jin wa’azi balle faÉ—a,haka nan babu wanda ya isa ya tunkaresu da niyyar gaya masu kuskurensu.
Dugun layine wanda yake shimfiɗe da lafiyayyan titi wanda ya ƙara fito da ƙyan unguwar.
Wasu jajaye fitilone sukaiwa titin unguwar ƙawanya,wanda a kullum suke haska unguwar musamman cikin dare,gefe da gefen titin wasu green flowers ne masu ƙyau wanda suke fidda wani daddaɗan ƙamshi.
Can kusan ƙarshen layin wani haɗaɗɗan gidane ginin zamani,tun daga jikin tafkeken get ɗin zaka san tabbas wannan gidan bana ƙana nan mutane bane,ajikin get ɗin anyi rubutu inda aka rubuta hause no 133.
Sosai harabar gidan taƙawatu da kurayan furanni na zamani masu ƙyau da tsari,Compound ɗin gidan cike yake da manyan motoci na zamani irinsu,boggatti,ferari,da sauransu.
Yanayin ginin gidan irin mai sama da Æ™asa É—inanne ma’ana dai ginin bene mai hawa biyu.
Side É—in parko na gidan wanda ya kasance hawan farko na gidan,babban parlour zaka fara tararwa gefen parlour’n kuma É—akuna ne masu É—an yawa kusan bedroom É—in shida,left hand É—ina nayi domin shine yafi jan hankalina fiye da sauran part É—in, Tun daga Æ™aramin parlour’n dake cikin part É—in na fara jiyo fitar numfashi mai kama dana zaucewa a hankali na tura kaina cikin bedroom É—in kasancewar a buÉ—e yake,saurin tsayawa nayi sabida ganin wata Æ™yaƙƙyawar matashiyar mata wacce aÆ™alla ba zata huce shekara ashirin da biyar ba zuwa shida.
Tana durƙoshe gaban bed ɗin dake ɗakin yayinda hannunta ke riƙe da gadon gaba ɗaya jikinta rawa yake,banda nishi da gurnanin wahala babu abinda ke fita a bakinta,yayinda turtsetsen cikinta ya sauka zuwa mararta banda juyawa da motsi babu abinda “ƊAN� cikin nata yake,da alamu shima ya ƙago yazo duniya,karkarwar jikin tane ya tsananta gaba ɗaya ta jigata ta fita haiyacinta banda kiran sunan Allah babu abinda bakinta yake ke faɗi,Can ƙasan zuciyarta kowa maganar data keson furtawa a saman bakinta tane ta kasa,burinta bai huce bakinta ya buɗe ta samu damar faɗin abinda ke damunta cikin rai da kuma zuciyarta,Runtsa idanunta tayi da ƙarfin sabida wani juyi da abin cikinta yay tare da naushin mararta nan take jini ya ɓalle mata ya soma zuba,cikin yanayin na fitar hayyaci tare da zaucewa haɗi da fidda rai ta ɓude baki da ƙyar tace.
“Ya hayyuu ya Æ™ayyumuu
ya kaliÆ™u ya zul arshidd majidd,ya fa’alulluma yurid biraha matika astagisuuu”
Takai Æ™arshen addu’ar tana sakin wani fitinanan nishi wanda ya kusa ta fiya da numfashinta ya rabbi nan take wani..
UNCLE NE complete hausa novel written by Ni’imerh Sulaiman Shu’aibu
Kamar amafarki Mameey dake ƙwance bisa tangamemen royal bed ɗinta ta jiyo sautin numfashin Zulfa cikin kunnuwanta lumshe idanu tayi tana jin kamar a magagin barci take, da sauri ta miƙe zaune daga ƙwancen da take wani irin hantsilawa Mameey tayi daga gadon zuwa ƙasan gadon,a gigice ta fara gyara ɗaurin zaninta dake kuncewa sabida fargaba,tabbas idan bata manta ba yaune E.D.D Zulfa ya cika gaba ɗaya ta manta,cikin tsoro fargaba kiɗima tashin hankali ta fara sakkowa daga stairs ɗin benen.
Tun a babban parlour ta fahimci aƙwai matsala kuma ta ƙara tabbatarwa kanta Zulfa naƙoda take da sassarfa ta ƙarasa shiga cikin part ɗin Zulfa,cikin sauri Mameey ta ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin,tana shiga ta samu Zulfa durƙoshe cikin jinin wanda ya ɓata jikinta gaba ɗaya,da sauri ta ƙarasa wajanta tana salati tare da faɗin.
“Zulfa mene zan gani haka?kika zauna cikin ciwo kin san illar duguwar naÆ™uda kowa?ohhh ni Salamatu yau naga abinda yafi Æ™arfina wannan wanne irin jinine haka?mun shiga uku”,
Ta faɗi hakan tana sakin kukan tausayi halin da Zulfan ke ciki,sabida ganin jinin dake zuba ta jikinta ga kuma yadda numfashinta ke sarƙewa jikinta banda rawa babu abinda yake,da hanzari ta ƙarasa matsawa inda take sabida kan babyn da taga yana fitowa,wata jijjiga Zulfa ta fara idanunta na kafewa.
Ganin hakan yasa Mameey sakinta tare da ficewa da gudu tana tafe tana ƙwala kiran sunan Alhaji!! Alhaji!! Alhaji!!!
Alhaji Kabeer na kishin giɗe saman wata lafiyayyiyar sofa,hannunsa dafe da saitin zuciyarsa,yana jin yadda take buga masa da ƙarfi,ga wani raɗaɗi da ɗaci daya keji a cikin maƙoshinsa,gefe guda kuma yana jin tsoro da fargaba haɗi da zullumi wanda bai san kona menene ba.
Ya rasa dalilin daya sanya yake mafalki mara ƙyau akan Zulfansa mace mafi soyuwa a cikin ransa,tabbas bazai jure ganinsa cikin wannan halin mafalkinba,kamar yadda bazai jure ganin Zulfa cikin wani hali ba.
Saurin buÉ—e idanunsa yay jin muryar uwar gidansa na kiran sunansa,da sauri ya dira daga kan sofar yana fita sukaci karo da Salmerh a birgice ya kalli Salmerh tare da faÉ—in..
“Salmerh mene ya sami Zulfa?..kada ki sake bakinki ya faÉ—i babban kalamai dazai sanya zuciyata bugawa..”
Bakinta na rawa tace
“Zulfa haihuwa inajin..”bai bari ta Æ™arasa maganar ba ya Æ™wasa da gudu zuwa part É—in Zulfa.
da gudu Mameey ta mara masa baya,suna zuwa tana haihuwa ganin zata danne jaririn ya sanya Alhaji Kabeer saurin isa gareta,yana zuwa ya saka hannu ya gyara mata zama,tare da amsar rezar hannun Mameey ya yanke cibiya,cikin ikon Allah a lkcn mahaifa ta faɗo,yana ganin haka ya saka hannu ya miƙar da ita tsaye cikin murna da farin ciki ya rungometa a jikinsa yana shafa sumar kanta idanunsa fal hawayen farin ciki,bai taɓa tunanin zai samu haihuwa nan kusa ba,sai gashi ubangiji ya azurtashi da ita a lkcn dabai taɓa tunanin samunta ba,tabbas ya yarda da wannan kalmar da ake cewa inda rai da rabo,haka kuma mutum baya fidda rai da samun rahamar ubangiji,domin shine mai bayarwa a lkcn da yaso haka kuma shine mai hanawa a lkcn dayaso,wasu hawayene suka fito daga cikin idanunsa cikin muryar farin ciki yace.
“Thank you soo much my Anuuu,Allah yay maki albarka nagode sosai da Æ™yautarki nagode Allah ina sonki Allah ya baki lafiya”
Mameey janye jaririn tayi jin yana tsala kuka a wani zani mai ƙyauta ta ɗaukesa,kana ta zaune bakin bed,catton da zaitun ta fara goge masa jiki da ita,murmushi tayi ganin yadda yake ƙoƙarin sanya hannu a baki da alama da yunwa yazo,sai tsala kuka yake,a cikin ranta take jinjina ƙyan yaron da kuma baiwar da ubangiji yay masa,domin ƙwayar idanunsa ta kasance blue ce,kamarta turawa,ga wani ɗan cindo a gefe yatsanshi.
A sanyaye Zulfa ta rungome mijinta Alhaji Kabeer idanunta na zubar da Æ™walla tace “Yaa rahamanu”murmushi yay tare da sumbatar goshinta,kamar an tsikareta ta sanya hannu ta ture Alhaji Kabeer daga jikinta,a hankali ta fara yin baya ganin hakan ya Æ™ara matsuwa kusa da ita yana shirin kamata yaji ta fasa wata uwar Æ™ara,a gigice ya Æ™arasa wajanta kafin ya riÆ™eta tasa hannu ta hankaÉ—esa tare dayin waje da gudu jinin haihuwa nabin jikinta….
Tsakure
Mama ta kalli Abbou tace “eyee haka akai bani da labari Kabeeru?, yaushe kai ma ka zama sallamamme wanda bai son laifin yaransa? Fisabilillahi ace samari manya kuma Æ™arti a gidanka amma kaÆ™i aurar dasu, a’a wlh wannan sangarta ce ban taÉ“a ganin inda akai wannan abun kunyar ba,da Æ™auye ne duk suna da yara Æ´an dugui dugui gwanin sha’awa”
Kafin Abbou yace komai Mameey tace
“Eyee! mata aka samawa yaron namu babu labari Abbou Jalal?”
Da ido Abbou ya kalleta ba tare kuma daya bata amsar maganarta ba ya kalli Mama yace
“Kiyi haÆ™uri in sha Allah da zarar komai ya lafa duk zasu lalubu matan auren”
Taɓe baki Mama tayi tace
“Dadai yafi,amma shi wancan basa mudan ai sai dai a sama masa,dan naga alama kamar ma tsoran matan yake,bazai iya tsayawa da mace har yace yana sonta ba,oh ohhh ohhhh banda ma zamani ina zaka kalli indon mutum kace kana sonsa kuma ya tsaya ai sai gudu,amma yanzu abin naga kamar wani gasa ne,haka jiya a talabijin naji ana ta faÉ—ar wani abu kai abindai sai dai su, hadda runguma fa”
Ta faɗa tana ɗan saka hannunta a haɓarta alamar mamaki
Murmushi Mummy tayi a zcyarta tace
“Tsofa labari”
A fili kuma tace
“Mama wannan ai É—ari’arsu ce haka,kinga Film É—in hausawanmu babu haka,so ko wanne yare aÆ™wai al’adar su da kuma É—abi’ar su,da ga Kennywood É—in zuwa India duk daban daban ne”
Mama ta ya tsuna fuska tace
“Tirr da wannan É—abi’ar mutane kamar tsirara” kafin ta kuma kallon Abbou tace
“Yawwa! Nace wacce mata ka zaÉ“awa Jalalun?”
Miƙewa Abbou yay ganin lokacin masallaci ya kusa yace
“Wata ce,soon za kiji komai ai”
Mama ta kwaɓe fuska tace
“Meya suun kuma?”
Aryan yay dry mai yawwa kafin yace
“Wai da wuri,ai Abbou daka faÉ—a mana domin mu fara shirin ganin Antyn tamu wacce tayi dacen samun zan kaÉ—eÉ—en saurayi irin yaya”
Abbou bai ƙara magana ba sai kallon Jalal da yay wanda ko inda suke bai kala ba bare su saka ran zai tanka maganarsu yace
“Muhammad lokacin masallaci yayi fa”
Idanunsa ya buɗe tare da saukesu akan Abbou bai ce komai ya miƙe tare da nufar part ɗinsa, Mama tace
“Allah É—aya gari babban”
Sarai yaji maganarta amma yay gaba abunsa, Aryan ma miÆ™ewa yay tare da shigewa nasa part É—in ya rage daga Mama sai Mummy da Mameey, Mameey tace “Mummyn Jalal me za’ai a gidanne yau?”
Mummy tace
“Haba Mameey duk abinda kikai dai-dai ne,tunda yau friday duk samarin gidan suna nan”
Kai Mameey ta É—aga tace
“Bari naje wajan Laure idan yaso taje anjima ta shigo,kin san indai tasa hannu to Jalal da Abbou Jalal baza su ci ba”
Tana faÉ—in hakan ta nufi hanyar kitchen Mummy kuma tayi upstairs part É—in su Jalilerh.
Jalal na shiga part É—insa ya nufa cikin bedroom kai tsaye ya shige cikin bathroom yana zare Æ´ar Æ™aramar singlet É—in jikinsa da kuma wando three gaiter daya saka, shower ya sakarwa kansa yana mai lumshe idanunsa,maganar Abbou ce ta faÉ—o masa,mai yasa har yanzu babu wanda yake Æ™oÆ™arin fahimtar abinda yake damunsa ne? Mene yasa har yanzu babu wanda zai iya tararsa ya tambaye sa dalilin yasa bai son yin aure? Ko kuma hakan da akai masa yana nuni da suna son suga hankalinsa ne? Wa zai aura? Zata iya fahimtar sa kamar yadda ya fahimci kansa? Zata iya zama dashi a haka? Ko kuma ba zata iya ba? Wanne kallo zatai masa idan ta san bazai iya biya mata buÆ™ata ba?zata raina sa ko kuma zata tausaya masa ne?mene dalilin daya sanya za’a takura rayuwarsa akan yay wani aure ne?
Yana da tabbacin sun san shi ba yaro bane indai yana buƙatar aure zaiyi ba tare da an takurasa ba
Babu wanda ya isa ya sanya shi yin aure ba tare da yay niyya ba,
Koda an tilasta shi yay auren, tabbas matar zata zama kayan wanki ne wanda basu da ranar wanke wa,
Iska ya fesar mai zafi ta cikin bakin lokacin guda yanayinsa ya sauya, shower ya kashe,tare da yin brush ya ɗaura alwala,yana fitowa ya nufi dressing mirror lotion ya shafa mai ɗan sauƙin zafi, tare da fesa body spray a saman fresh skin ɗinsa,wajan wardrobe ya nufa wata shadda majic ya ɗauka mai kalar sky blue tare hula mai kalar light blue,cikin sauri yake komai sbd ganin lokacin na neman yanke masa,black half shoe ya sanya,tare da ɗaukan paryaer mat ya fita a ɗakin
Yana fita parlour yaga babu kowa kai tsaye ya shige part É—in Mama zaune ya sameta tana faman daka goro, a kanta ya tsaya tare dayin shuru yana tunanin ta inda zai fara,dan idan yace cikin É“acin rai zai magana za’a iya samun matsala sbd gaba É—ayansa jinsa yake a sama zcyarsa banda tafasa babu abinda take,ba yajin a yanzu zai iya control kansa amma ya zame masa wajibi daya saita kansa, Mama ta taÉ“e baki tace
“Ayee mama ayeee mama mayeee iyeee,ayeee mama labu labu mama yeee iyeee”
Haɗe rai shima yay kafin yay ƙasa da murya yace
“Ina yini”
Cikin ƙufula Mama tace
“Kaji ance bani da lafiya ne Muhammad? Da ban yini da lafiya ba aida ka samu labari wajan ubanka”
Cije lips yay kana ya zamu daga saman sofa yace
“Haba matar,laifin me mijin yayi ne”
Taɓe baki tayi tare da watsa dakakken goran a baki tace
“Uhmm duniyyanci kenan,Ni za’ai wa sanabe”
Zamuwa yay daga saman sofar gaba ɗaya ya ƙarasa inda take zaunan ya cire hular kansa tare da ɗura kan a saman cinyarta,shuru tayi tana ɗan sauke ajjiyar kafin tasa tafin hannunta a saman sumar kansa ta shafa a hankali tace
“Nayi kewar jikana kuma mijina”
ÆŠago kai yay tare da zubawa Mama Idanu wajan 3minutes yace
“Mama mene yasa kikeson dole sai nayi aure ne?”
Washe baki tayi tace
“Kai É—aya kai ne jikana na miji,sai Æ™aramar Æ™anwarka Ina son naga ka sama min yara,ina da burin naga ka tara zuri’a masu yawan gaske kuma masu albarka,bana son yadda ban tara iyali ba ace kaima haka tara ba,wannan dalilin ya sanya nake burin naga kayi aure kafin Æ™asa ta rufe idona,kullum cikin mafarkai nake wanda bana gane kansu ina jin tsoro dan ban san dalilin wannan mafarkan ba,kaji dalili nason naga ka ajjiye zuri’a”
Ɗago jajayen idanunsa yay yana mai kallon Mama, lokacin guda zuciyarsa ta bada sauti damm Tabbas asiri sa yana gaf da tunuwa, rauninsa yana shirin bai yana abinda ko a mafarki baya fatan ace hakan ya kansace,abinda bashi da ikon faruwarsa haka kuma bashi da ikon hana faruwarsa, ƙaddara juyi juyi ce tana maida mai ƙyau ya zama mara ƙyau ko kuma ta mayar da mara ƙyau ya zama mai ƙyau,yana da yaƙi nin tasa ƙaddarar zata juya daga mara ƙyau ta dawo mai ƙyau,yaushe? Da wanne lokacin? Shine abinda bai sani ba,runtsa idanunsa yayi yana sauraran bugun zcyarsa dake fita da sauri da sauri wayarsa take cikin aljihu ce ta fara ƙara, miƙewa yayi sbd yasan kiran daga wane kai tsaye ya fice daga ɗakin idanunsa rufe, Mama ta bisa da kallo tare da tafa hannayenta tace
“Ohhh ni Abu ina za’a biyewa wannan yaron,dole sai an nema masa taimako Æ™ilan wata baÆ™ar aljanarce ta aureshi..,”
Sai kuma tasa hannu da sauri ta rufe bakinsa tana juyawa tare da ƙare wa ɗakin kallo tamkar wacce taga aljanar a gabanta.
A main parlour ya samu Abbou tsaye shida samarin gidan,kamar haÉ—in baki duk shadda iri É—aya suka saka babu bambanci hadda Abbou.
Imran yace
“Abbou lokaci na tafiya” gaba Abbou yayi Irfan da Imran suka take masa baya sai kuma Aryan na ukunsu,har suka fice daga cikin gidan Jalal na tsaye yana kallon su, Irfan ya kula Jalal bai taho ba ya juya baya a hankali ya hangesa yana tafiya lokacin daya iso wajan har sun shiga mota, Aryan a motar sa da Imran a gaba sai Irfan a bayan motar, Jalal shi kuma ya nufi motar da Abbou ya shiga ya zauna a back seat kusa Abbou,sai kuma motar securities É—insa ta rufa masu baya,misalin 1:30 suka isa harabar babban masallacin juma’ar jama’a sai É—agawa motar Jalal hannu suke, yana daga cikin motar yake kallon kowa É—ai-É—ai har suka Æ™arasa wajan parking,sahun farko Jalal ne tsaye bayansa kuma Æ´an uwansa gefensa kuma Mahaifinsa a haka sukai sallar har aka idar,ana idarwa kowa ya fara tashi, Abbou hannun Jalal yaja suka nufi Æ™ofar baya sabida dubban jama’ar da suka tare Æ™ofa suna jiran fitowar sa,a haka suka Æ™arasa wajan motocin su ba tare da angansu ba,kai tsaye suka nufi gida,tun a hanya aka fara sakin breaking news a gidan t.v da gida redio akan
Governor Muhammad Jalal Kabeer bobo mai neman takarar kujerar Gwamna a jam’iyyar D.R.P ya hallarci sallar juma’a shida danginsa
A ka rubuta hakan tare da photonan sa dana ƴan uku, da yawanci photonan wasu ne sukai masa a wajan,duk halin da yake na ƙunci da rashin sukuni bai hana shi yin wani lafiyayyan murmushi ba,hannu yasa yaja sajen fuskarsa kana yayi baya tare da lafewa jikin kujerar yana sauke ajjiyar zcy.
Da yamma wajan biyar da rabi governor Mubarak Yahya cibo ne zaune gaban wani mutumi dake sanye da wasu jajayen kaya jikinsa duk anyi rubutu da jan fenti, idanunsa manyan manya wanda ƙwayar cike ta kasance jajir tamkar zata zubar da jini,gabansa ƙasa ce da kuma wasu manyan ƙoƙuna,dariya bokan yay yace
“Kana cikin halaka wacce idan kayi sake ta faÉ—a maka ka shiga uku babu mai iya cireka daga cikin ta, abubuwa da yawa suna shirin faruwa amma ba zaiyu na faÉ—a maka yanzu ba,sai dai abu guda zakai wanda zaka iya tseratar da kujerarka da kuma mutuncinka,idan kai hakan babu shakka zaka daumawa ne tare da kujerarka babu wani wanda ya isa ya karÉ“a daga wajanka”
Mubarak Yahya cibo jikinsa na rawa yace
“Na maka al’Æ™awarin ko mene zan aikata dukkan abinda kake so zan baka muddin ba rayuwata ka nema ba,burina ni bai huce a dauwamar dani a matsayin zaÉ“aɓɓe kuma shugaban dake wakilan wannan yankin na IBADAN ba,na mulki kowa na juya kowa yadda nakeso,na zama shararre tako wanne É“angare”
Boka Saƙib yace
“Abubuwa uku muke nema wajanka,biyun farko buÆ™atun aljanu ne wanda suka saba maka aiki,na ukun kuma buÆ™ata tace,domin aikin da zan maka ba Æ™arami bane zan sanya kaina cikin hatsari,Amma muddun ka biyamu abin da muka É“ukata kai da mulki sai mutuwa”
Jikin Mubarak Yahya cibo yana rawa yace
“FaÉ—i abinda kake so zan baka,ko mene shi kuma komai girmansa”
Boka Saƙib yayi wata mahaukaciyar dry nan take wani hayaƙi ya fara fita ta cikin bakinsa,wajan mintuna biyar sannan yayi shuru tare da tsuke fuskarsa yace
“Muna buÆ™atar jarirai guda biyar sabbin haihuwa,sai kuma idanun yara masu wayo guda biyu…,”
Shuru yay na wani lokaci kafin ya É—ora da faÉ—in
“BuÆ™ata ta Æ™arshe kai da matarka muke buÆ™ata,zanyi amfani dakai kuma zanyi amfani da matarka ne bayan kaci zaÉ“en”
Cikin hanzari Mubarak Yahya cibo ya ɗaga kai ya kalli boka Saƙib kana ya maida kan zuwa ƙasa yace
“Ban gane mene kake son faÉ—a ba”
Wangalelen bakinsa bokan ya buÉ—e yace
“Ina nufin zanyi amfani dakai ma’ana zamuyi luwaÉ—i (Astagafirullah) sannan idan kaci zaÉ“en zaka kawo min matarka na Æ™wanta da ita,wannan bawai shawararka nake nema ba kusan dole ne sabida ka riga ka aminci da abinda nace tun kafin na gaya maka abubuwan da muke buÆ™ata,idan kaÆ™i kuma zaka kaga abinda zai faru da kai”
Tunani Mubarak Yahya cibo ya fariyi,shin boka Saƙib nada cuta ko bai da ita? Kullum zasu dinga aikata hakan ko kuma na wani lokaci ne,sannan idan yaci zaɓen zai iya ƙin kawo masa matar tasa sbd burinsa ya riga daya gama cika bashi da ikon da zai sanya a ƙwace masa mulkinsa, numfashi ya sauke kana yace
“BuÆ™atar ka a gareni na yini guda ne? Ko kuma na wasu ranaku ne?”
Zane boka Saƙib yayi a jikin ƙasa kafin ya ɗago kai yace
“Na Sa’a biyu ne kacal,da zarar mungama shikenan ka gama aikinka sai bayan zaÉ“e”
Murmushi Mubarak Yahya cibo yayi yana mai jin wani farin ciki tare da anushuwa a cikin zcyarsa, gani yake tamkar ya yaci wannan zaÉ“en ne hakan tasa cikin sauri yace “na amince..
UNCLE NE complete hausa novel written by Ni’imerh Sulaiman Shu’aibu
Source
Just to let you Know that all musics files appeared or discovered on our website are from third Party sites, so we dont owned or controlled them we only shared them by link, the only internal files we shared is Ebook, to know more about our policy pls see our Privacy Policy page.
Also Download SABON AL’AMARI complete hausa novel written by Bilyn Abdul
Download
Kindly click the below button to download, pls in case you get trouble trying to download kindly drop a comment.
Comments
Post a Comment